A ci gaban ziyarar jami'an diplomasiyya a lardin Jiangsu na kasar Sin, a jiya Talata ne jami'an diplomasiyya suka isa birnin Taizhou da ke tsakiyar lardin Jiangsu, inda magajin garin birnin Mr. Shi Lijun ya karbe su da hannu bibbiyu, ya kuma yi musu takaitaccen bayani game da birnin, tare kuma da fatan jami'an za su fadakar da kasashensu, game da wannan birni mai ni'ima. (Lubabatu)